99. The Earthquake

1
إِذَا زُلْزِلَتِ الْأَرْضُ زِلْزَالَهَا
Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.
2
وَأَخْرَجَتِ الْأَرْضُ أَثْقَالَهَا
Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.
3
وَقَالَ الْإِنسَانُ مَا لَهَا
Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"
4
يَوْمَئِذٍ تُحَدِّثُ أَخْبَارَهَا
A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.
5
بِأَنَّ رَبَّكَ أَوْحَىٰ لَهَا
cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.
6
يَوْمَئِذٍ يَصْدُرُ النَّاسُ أَشْتَاتًا لِّيُرَوْا أَعْمَالَهُمْ
A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.
7
فَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ خَيْرًا يَرَهُ
To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.
8
وَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ شَرًّا يَرَهُ
Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.
CopyRight © 2024 Koran.link All Rights Reserved