93. The Forenoon

1
وَالضُّحَىٰ
Inã rantsuwa da hantsi.
2
وَاللَّيْلِ إِذَا سَجَىٰ
Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).
3
مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ
Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.
4
وَلَلْآخِرَةُ خَيْرٌ لَّكَ مِنَ الْأُولَىٰ
Kuma lalle ta ƙarshe ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.
5
وَلَسَوْفَ يُعْطِيكَ رَبُّكَ فَتَرْضَىٰ
Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.
6
أَلَمْ يَجِدْكَ يَتِيمًا فَآوَىٰ
Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?
7
وَوَجَدَكَ ضَالًّا فَهَدَىٰ
Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?
8
وَوَجَدَكَ عَائِلًا فَأَغْنَىٰ
Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?
9
فَأَمَّا الْيَتِيمَ فَلَا تَقْهَرْ
Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.
10
وَأَمَّا السَّائِلَ فَلَا تَنْهَرْ
Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.
11
وَأَمَّا بِنِعْمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثْ
Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).
CopyRight © 2024 Koran.link All Rights Reserved