82. The Cleaving

1
إِذَا السَّمَاءُ انفَطَرَتْ
Idan sama ta tsãge.
2
وَإِذَا الْكَوَاكِبُ انتَثَرَتْ
Kuma idan taurãri suka wãtse.
3
وَإِذَا الْبِحَارُ فُجِّرَتْ
Kuma idan tẽkuna aka facce su.
4
وَإِذَا الْقُبُورُ بُعْثِرَتْ
Kuma idan kaburbura aka tõne su.
5
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا قَدَّمَتْ وَأَخَّرَتْ
Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.
6
يَا أَيُّهَا الْإِنسَانُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ الْكَرِيمِ
Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci.
7
الَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّاكَ فَعَدَلَكَ
Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.
8
فِي أَيِّ صُورَةٍ مَّا شَاءَ رَكَّبَكَ
A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.
9
كَلَّا بَلْ تُكَذِّبُونَ بِالدِّينِ
A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!
10
وَإِنَّ عَلَيْكُمْ لَحَافِظِينَ
Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.
11
كِرَامًا كَاتِبِينَ
Mãsu daraja, marubũta.
12
يَعْلَمُونَ مَا تَفْعَلُونَ
Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.
13
إِنَّ الْأَبْرَارَ لَفِي نَعِيمٍ
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima.
14
وَإِنَّ الْفُجَّارَ لَفِي جَحِيمٍ
Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.
15
يَصْلَوْنَهَا يَوْمَ الدِّينِ
Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako.
16
وَمَا هُمْ عَنْهَا بِغَائِبِينَ
Bã zã su faku daga gare ta ba.
17
وَمَا أَدْرَاكَ مَا يَوْمُ الدِّينِ
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rẽnar sakamako?
18
ثُمَّ مَا أَدْرَاكَ مَا يَوْمُ الدِّينِ
Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako?
19
يَوْمَ لَا تَمْلِكُ نَفْسٌ لِّنَفْسٍ شَيْئًا ۖ وَالْأَمْرُ يَوْمَئِذٍ لِّلَّهِ
Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake.
CopyRight © 2024 Koran.link All Rights Reserved