96. The Clot

1
اقْرَأْ بِاسْمِ رَبِّكَ الَّذِي خَلَقَ
Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.
2
خَلَقَ الْإِنسَانَ مِنْ عَلَقٍ
Ya hahitta mutum daga gudan jini.
3
اقْرَأْ وَرَبُّكَ الْأَكْرَمُ
Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.
4
الَّذِي عَلَّمَ بِالْقَلَمِ
Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.
5
عَلَّمَ الْإِنسَانَ مَا لَمْ يَعْلَمْ
Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.
6
كَلَّا إِنَّ الْإِنسَانَ لَيَطْغَىٰ
A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).
7
أَن رَّآهُ اسْتَغْنَىٰ
Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.
8
إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ الرُّجْعَىٰ
Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.
9
أَرَأَيْتَ الَّذِي يَنْهَىٰ
Shin, kã ga wanda ke hana.
10
عَبْدًا إِذَا صَلَّىٰ
Bãwã idan yã yi salla?
11
أَرَأَيْتَ إِن كَانَ عَلَى الْهُدَىٰ
Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?
12
أَوْ أَمَرَ بِالتَّقْوَىٰ
Ko ya yi umurni da taƙawa?
13
أَرَأَيْتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?
14
أَلَمْ يَعْلَم بِأَنَّ اللَّهَ يَرَىٰ
Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?
15
كَلَّا لَئِن لَّمْ يَنتَهِ لَنَسْفَعًا بِالنَّاصِيَةِ
A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.
16
نَاصِيَةٍ كَاذِبَةٍ خَاطِئَةٍ
Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.
17
فَلْيَدْعُ نَادِيَهُ
Sai ya kirayi ƙungiyarsa.
18
سَنَدْعُ الزَّبَانِيَةَ
Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).
19
كَلَّا لَا تُطِعْهُ وَاسْجُدْ وَاقْتَرِب ۩
A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).
CopyRight © 2024 Koran.link All Rights Reserved