105. The Elephant

1
أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِأَصْحَابِ الْفِيلِ
Ashe, ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ga mutanen giwa ba?
2
أَلَمْ يَجْعَلْ كَيْدَهُمْ فِي تَضْلِيلٍ
Ashe, bai sanya kaidinsu a cikin ɓata ba?
3
وَأَرْسَلَ عَلَيْهِمْ طَيْرًا أَبَابِيلَ
Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a.
4
تَرْمِيهِم بِحِجَارَةٍ مِّن سِجِّيلٍ
Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta.
5
فَجَعَلَهُمْ كَعَصْفٍ مَّأْكُولٍ
Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye?
CopyRight © 2024 Koran.link All Rights Reserved